News
Gwamnatin jahar Kano Ta Kaddamar Da Kwamitin Tantance Ma’aikata Kusan Dubu 10 da 800
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Gwamnatin jihar Kano ta kafa kwamitin mutum 22 domin tantance ma’aikata kusan dubu 10 da 800 da aka dauka aiki a karshen wa’adin gwamnatin da ta gabata ta Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Sakataren gwamnatin jihar Kano, Dr. Baffa Bichi, ya ce kwamitin zai tabbatar da ko anbi ka’ida wajen daukar ma’aikata kusan dubu 10 da 800.
Gwamnatin Kano Ta Bayyana Damuwa Kan Yunkurin Bada Cin Hanci A Kotun Kararrakin Zabe
Kwamitin zai yi aiki bisa jagorancin shugaban hukumar daukar ma’aikata, Alhaji Umar Shehu Minjibir, kuma an baiwa kwamitin wa’adin makonni uku ya kammala aikinsa.
A martanin da ya mayar, Minjibir ya yi alkawarin cewa mambobin kwamitin za su yi iya kokarinsu don ganin sun kammala aikin a kan lokaci.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
