News
Shetima zai yi balaguro zuwa kasar Afrika ta kudu
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shetima zai yi balaguro zuwa birnin Johannesburg na kasar Afrika ta kudu, domin wakiltar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a taron Shugabannin kungiyar kasashen BRICS karo na 15.
Daraktan yada labarai na ofishin mataimakin shugaban kasa, Olusola Abiola ne ya baiyana haka ta cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin a Abuja.
Peter Obi Ya Musanta Cewar Yana Tattaunawa Da Kwankwaso Da Atiku Domin Kafa Sabuwar Jam’iyya
Mataimakin shugaban kasar zai bi sahun sauran shugabannin kasashe da ‘yan kasuwa da kuma ‘yan siyasa daga sassa daban daban na duniya a yayin taron da za’a yi a cibiyar taro ta Sandton dake birnin Johannesburg daga yau 22 ga wata zuwa 24 ga watan da muke ciki.
Taron kasashen kungiyar BRICS, ya kunshi kasashen Brazil da Rasha da India sai China da Afrika ta kudu wanda suka cure wuri daya a kokarin da inganta tattalin arzikin duniya.
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
-
News3 days ago
Uba Ya Nemi Kotu Ta Tilasta Wa ’Yarsa Ta Fitar Da Mijin Aure A Kaduna
