News
Mutane 140 ne suke jira a zartar musu da hukuncin kisa a Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar da ke kula da gidajen gyaran hali ta Jihar Kano a arewacin Nijeriya ta ce mutum dari da arba’in ne suke jira a zartar musu da hukuncin kisa bayan kotuna sun same su da laifuka.
Kakakin hukumar, Musbahu Kofar-Nassarawa ne ya bayyana haka ranar Asabar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Kasa (NAN) ya rawaito.
Ya kara da cewa mutanen sun hada da maza da mata.
Ɗan wasan baya na Portugal Pepe ya kafa sabon tarihi a gasar Zakarun Turai
“Hukumar da ke kula da gidajen gyaran hali ta Kano ba ta da mai rataye mutane saboda wuri ne na daure mutanen da suka aikata matsakaitan laifuka,” in ji Kofar-Nassarawa.
Ya kara da cewa gwamnonin da suka mulki jihar sun gaza sanya hannu kan takardun zartar da hukuncin kisa ko kuma su mayar da hukuncin na daurin rai-da-rai.
“Wasu gwamnonin suna amfani da damar da kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba su domin sakin mutanen da ke kurkuku bisa samun shawarwari daga Majalisar Bayar Da Shawara kan yi wa fursunoni afuwa domin rage cunkoso a gidajen yari,” a cewar Musbahu Kofar-Nassarawa.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
