Connect with us

News

Gobara ta kone shaguna a jihar Jigawa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Akalla shaguna uku da wasu kayayyaki masu daraja na miliyoyin naira ne suka kone a ranar Juma’a sakamakon gobara da ta tashi a unguwar kasuwar Bakin da ke karamar hukumar Hadejia a jihar Jigawa.

DSC Adamu Shehu, kakakin hukumar tsaron farin kaya ta kasa (NSCDC) a jihar ya tabbatar da faruwar lamarin a Dutse ranar Asabar kamar yanda Jaridar Daily News24 ta ruwaito 

Kotu ta yanke wa Sarkin Fulani, Usman daurin rai da rai

Shehu ya ce gobarar ta kone kantuna uku da rumfa da wani bangare na wani masallaci a yankin

“A ranar Juma’a da misalin karfe 10:30 na rana, ofishin hukumar NSCDC reshen Hadejia ya samu kiran wayar tarho game da gobarar da ta tashi a rukunin shagunan Na Malam Zangi da ke Bakin Kasuwa, babbar kasuwar Hadejia.

Advertisement

“Nan da nan aka tura tawagar jami’an bayar da agajin gaggawa zuwa wurin domin kashe gobarar tare da ceto dukiyoyin da ba a kone ba tare da kiyaye sata.

Ya bayyana cewa har yanzu ba a gano takamammen hanyar da wutar ta tashi ba.

Kakakin hukumar NSCDC, ya ce wanda lamarin ya faru a kan idonsa, ya yi ikirarin cewa gobarar ta tashi ne daga wata wutar lantarki da ke kusa da daya daga cikin shagunan.

Shehu ya ce, an kashe gobarar ne da hadin gwiwar jami’an NSCDC, hukumar kashe gobara, da mazauna yankin.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending