Connect with us

News

An Samu Rahotannin Hatsari Kimanin 231, Yayin Da Mutane 205 Suka Mutu A Jihar Kano

Published

on

Advertisements
ads

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Hukumar kiyayye haddura ta kasa, tace ta samu rahotannin hatsari kimanin 231, yayin da mutane 205 suka mutu a jihar Kano kadai, daga watan Janeru zuwa Nuwambar wannan shekarar.

Shugaban hukumar na Jihar Ibrahim Abdullahi,shine ya sanar da haka ga kamfanin dillancin labarai na kasa a Kano.

Jam’iyyun APC da NNPP Sun Koma Ga Allah Yayin Da Kotun Koli Zata Fara Sauraren Karar Zaben Gwamnan Jihar 

Ibrahim Abdullahi,yace kimanin mutane 1,451 ne haddura ya rutsa da su, yayin da mutane sama 759 suka samu muna-nan raunuka, inda hukumar ta samu nasarar ceto mutane 692 da sukayi hatsari.

 

Ya kara da cewa kimanin ababan hawa 33,324 suka kwace sakamakon keta dokokin amfani da hanya.

Advertisement

 

Ya bayyana wasu daga cikin laifukan da suka aikata kamar,rashin mallakar lasisin tuki, lodin da wuce kima da kuma gudun wuce gona da iri. Shugaban hukumar a Jihar Kano,ya bukaci masu amfani da motoci suna kiyaye dokokin hanya tare da yin amfani da Danjar da ke tsayar da ababan hawa domin tabbatar da lafiyar mutane akan hanya.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending