News
Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun yi awon gaba da wasu masallata cikin masallacin a Zamfara.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun yi awon gaba da wasu masallata a ɗaya daga cikin masallacin da ke garin Tsafe hedikwatar ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.
Wani ɗan yankin mai suna Garba ya bayyana cewa ƴan bindigar sun mamaye masallacin ne da misalin karfe 5 na safiyar ranar Alhamis a lokacin da mutanen ke shirin fara Sallar Asuba.
Kada ku rasa wannan damar, saka hannun jari Yanzu A company BAHAL DATA Ga dama ta samu
Garba ya ce, “Yau alhamis muna shirin tada sallar asuba, kwatsam sai ga yan bindiga sun dira masallaci inda suka umurci duk jama’an ciki su biyo su inda Ni na yi nasarar ɓoyewa ba su ganni ba.”
Ya ƙara da cewa saboda kar a ji karar abin bawan su sai suka ajiye Baburan su can nesa.
A ƙalla mutane 30 ne aka yi awon gaba da su.
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
-
News5 days ago
Kwamitin Tsara Kundin Yakin Neman Zaɓen Gwamnan Kano Ya Yi Taron Tsare-tsare Manufofin Ci Gaban Jihar A Kaduna
