News
Gwamnatin Tarayya Ta Tsawaita Ranakun Hutun Karamar Sallah
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin Tarayya ta amince da sanya Alhamis, 11 ga watan Afrilun 2024 a cikin jerin kwanakin hutun karamar sallah da ta bayar.
Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida, Dokta Olubunmi Tunji-Ojo ya fitar a safiyar wannan Talatar.
Wannan na zuwa ne sakamakon rashin ganin jinjirin watan Shawwal a jiya Litinin da zai kawo ƙarshen watan Ramadan.
Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariya a Ma’ikatar Harkokin Cikin Gida, Dokta Aishetu Gogo Ndayako, tana kuma taya al’ummar Musulmi kammala Azumin watan Ramadana lafiya tare da fatan Allah Ya karɓi ibadu.
Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Lahadin da ta gabata ce Gwamnatin Tarayya ta ayyana wannan Talatar da gobe Laraba a matsayin ranakun hutun sallah karama a faɗin Najeriya.
Sai dai kuma a sakamakon rashin ganin watan Shawwal ne Majalisar Ƙolin Musulunci ta Nijeriya ta ayyana Laraba a matsayin ranar bikin sallah.
Gwamnatin Tarayya dai ta saba bayar da kwanaki biyu ne a matsayin ranakun hutun sallah domin ma’aikata da sauran al’ummar ƙasar.
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News14 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
