News
Masu garkuwa da mutane sun bindige Farfesan Jami’ar Babcock tare da yin garkuwa da wasu mutane biyu
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe Farfesa Yinka Olomojobi, farfesa a fannin shari’a a jami’ar Babcock da ke Ilisha a jihar Ogun, tare da yin garkuwa da wasu mutane biyu.
Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da maharan suka mamaye yankin Iperu na jihar.
Harin Yan Bindiga Ya Sa Al’ummar Bini Gudun Hijira Zuwa Fadar Gwamnatin Jihar
Masu garkuwa da mutanen, kamar yadda rahotanni suka bayyana, sun yi niyyar sace Olomojobi, amma an harbe shi har lahira .
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an kama mutum guda da hannu a lamarin.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
