News
Babbar Magana: Barawo Ya Sace Sadaki Ana Shirin Daurin Aure A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wani barawo da ba a kai ga gano shi ba ya sace sadaki a aljihun wakilin Ango a yayin daurin aure a masallacin Juma’a na Usman Bin Affan dake Gadon Kaya.
Rahotanni na nuni da cewa babban limamin Masallacin, Sheikh Aliyu Yunus ya gano hakan yayin da aka bukaci wakilin Angon ya gabatar da Sadakin inda aka nemi kudin aka rasa.
Wata majiya mai tushe ta shaidawa Jaridar Nigerian Tracker cewa wakilin Angon ya bada hakuri inda ya nemi limamin ya daura auren tare da alkawarin kawo sadakin daga baya.
A addinin Musulunci dai an amince da daura aure yayin da aka bada Sadaki nan take ko a ka dau alkawarin bayarwa daga baya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
