Connect with us

News

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga A Borno, Filato Da Kaduna

Published

on

images 2022 12 26T181354.825 715x375

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro sun kashe ‘yan bindiga sannan sun kama wani mai safarar makamai dake da alaka da wani mashahurin dan bindiga da jami’an tsaro ke nema ruwa a jallo.

A ranar 3 ga Satumba dakarun dake samar da tsaro a karamar hukumar Gwoza dake jihar Borno sun afka wa ƴan bindiga dake tsaunukan Mandara. Dakarun sun ceto mutum 24 da maharan suka yi garkuwa da su bayan nasara da suk yi a kansu.

Man Fetur Din Dangote Zai Fara Isa Kasuwa Makon Gobe  – Kamfanin  NNPC

Sojojin sun kwato bindigogi da harsasai ma su yawa.

Daga nan a jihar Kaduna kuma  dakarun sun kashe wani hatsabibin dan bindiga a kauyen Kabode dake karamar hukumar Kachia sai dai sauran ƴan bindigan sun gudu.

Dakarun sun ceto mutum hudu da maharan suka yi garkuwa da su sannan sun kwato AK-47 daya, harsasai 10, babura shida da wayoyin hannu uku.

Advertisement

“Dakarun tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro sun kai hari tsaunin Keyeri da Gidan Dogo dake karamar hukumar Kagarko a jihar Kaduna inda suka kama wani dake safarar makamai wa mahara a dakin Gidan Dogo.

“Dakarun sun kwato bindiga kirar AK-47 uku, bindiga kirar Galil daya da harsasai da dama.

“Binciken da jami’an tsaron suka gudanar kan mai safarar muggan makaman ya taimaka wajen kama wasu masu safarar makamai 8.

Bayan haka dakarun dake samar da tsaro a jihar Filato sun kai farmaki a maboyar mahara a karamar hukumar Riyom inda har suka kama ‘yan bindiga biyu sannan sun kwati wayoyin hannu biyu da wuka.

 

 

Advertisement

PREMIUM TIMES

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending