Connect with us

News

Man Fetur Din Dangote Zai Fara Isa Kasuwa Makon Gobe  – Kamfanin  NNPC

Published

on

Matatar Man Dangote ta zargi hukumar NUPRC da gazawa wurin gudanar da ayyukanta

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

Kamfanin man fetur din Najeriya (NNPC) ya bayyana cewa man fetur din matatar Dangote zai fara isa kasuwa tun daga ranar 15 ga watan Satumba mai kamawa.

Advertisement

Kamfanin wanda ya bayyana hakan a sanarwar da babban jami’in yada labaransa, Olufemi Soneye ya fitar a jiya Alhamis a Abuja, tace kasuwa da kanta ce zata yanke farashin da za a sayar da man.

Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnatin Tarayya Mai Rahusa 

Hakan dai ya biyo bayan fara tace man fetur din da matatar ta Dangote tayi a farkon makon nan.

Advertisement

Da yake ruwaito kalaman mataimakin shugaban bangaren cinikayyar albarkatun man kamfanin NNPC, Adedapo Segun, Soneye yace an kammala cefanar da bangaren cinikayyar kamfanin don haka bashi da sauran hakkin yanke farashi.

Kalaman nasa sun kawo karshen rade-raden da ake yi na cewar NNPC zai cigaba da yanke farashin albarkatun man fetur

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending