News
Jami’ar Dangote Za Ta Ba Da Digirin Girmamawa Ga Kwankwaso, Mangal, AMMASCO Da Sauransu
Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil, Jihar Kano, ta ce za ta ba da digirin girmamawa ga wasu fitattun ’yan Najeriya sakamakon gudummawar da suka bayar wa kasa.
Shugaban jami’ar, Farfesa Musa Yakasai ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar kafin bikin yaye dalibai da za a fara ranar Laraba.
NDLEA Ta Kama Masu Safarar Kwayoyi Fiye da 62,000 A Najeriya
Cikin wadanda za a ba digirin girmamawa akwai Alhaji Dahiru Mangal, Chief Author Eze, Dr. Adeniyi Raji (SAN), Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da kuma Alhaji Mustapha Ado Muhammad (AMMASCO).
Farfesa Yakasai ya ce an zaɓi mutanen ne bisa la’akari da halayensu da kuma irin ayyukan jin ƙai da suke yi a cikin al’umma.
Ya kara da cewa dalibai 18,000 da suka kammala karatu a cikin shekaru bakwai da suka gabata za a yaye su a lokacin bikin.
Haka kuma ya tabbatar da cewa jami’ar ta ɗauki matakan tsaro domin kare lafiyar mahalarta da dukiyoyinsu.
Farfesa Yakasai ya ce za a sake naɗa Alhaji Aliko Dangote a matsayin Chancellor na jami’ar a karo na biyu, yayin da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf zai kasance baƙon musamman na jami’ar a lokacin bikin.
Ya yaba da goyon bayan da gwamnatin jihar ta bayar domin ganin an gudanar da bikin lafiya lau.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
