Connect with us

News

Gwamnan Kano Ya Kori Baffa Bichi Da Sagagi Da Wasu Kwamishinoni Guda 5

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnan Jihar Kano, Alh. Abba Kabir Yusuf, ya sanar da sake fasalin majalisar zartarwa ta jihar domin tabbatar da daidaituwar harkokin siyasa a gwamnatinsa.

A wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar a ranar Alhamis, Gwamna Yusuf ya bayyana cewa wannan babban canji na farko a majalisar zartarwarsa ya fara aiki nan take.

DA DUMI-DUMI : Gwamna Abba Kabir Ya Kori Wasu Daga Cikin Kwamishinan Sa

Daga cikin wadanda canjin ya shafa sun hada da Shugaban Ma’aikata, Alh. Shehu Wada Sagagi, wanda aka soke ofishinsa, da kuma Sakataren Gwamnatin Jiha, Dr. Abdullahi Baffa Bichi, wanda aka cire saboda matsalolin lafiya.

A cewar Sanusi Bature Dawakin-Tofa, Gwamna Yusuf ya sauke wasu mambobin majalisar zartarwa sannan ya mayar da wasu zuwa wuraren da za su inganta aikin mulki jihar.

Daga cikin wadanda suka ci gaba da rike mukamansu akwai:

Advertisement

 

Antoni Janar kuma Kwamishinan Shari’a, Bar. Haruna Isa Dederi,

 

Kwamishinan Noma, Dr. Danjuma Mahmoud,

 

Kwamishinan Lafiya, Dr. Abubakar Labaran,

Advertisement

 

Kwamishinan Filaye da Tsare-tsare, Hon. Abduljabbar Mohammed Umar,

 

Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsare, Hon. Musa Suleiman Shannon,

 

Kwamishinan Ayyuka da Gidaje, Injiniya Marwan Ahmad.

Advertisement

 

 

Haka zalika, wadanda suka ci gaba da rike mukamansu sun hada da:

 

Kwamishinan Albarkatun Ma’adanai, Sefiyanu Hamza,

 

Advertisement

Kwamishinan Harkokin Addini, Sheikh Ahmad Tijjani Auwal,

 

Kwamishinan Matasa da Wasanni, Hon. Mustapha Rabiu Kwankwaso,

 

Kwamishinan Zuba Jari da Kasuwanci, Adamu Aliyu Kibiya,

 

Advertisement

Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Sabis na Musamman, Manjo Janar Mohammad Inuwa Idris (mai ritaya).

An mayar da wasu zuwa sabbin ma’aikatun da suka hada da:

 

Mataimakin Gwamna, Kwamared Aminu Abdulssalam, daga Ma’aikatar Kananan Hukumomi zuwa Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi,

Hon. Mohammad Tajo Usman daga Kimiyya da Fasaha zuwa Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta,

 

Advertisement

Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata daga Ilimi Mai Zurfi zuwa Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire.

 

Sauran sun hada da:

 

Hon. Amina Abdullahi daga Jin Kai da Rage Talauci zuwa Ma’aikatar Mata, Yara da Nakasa,

 

Advertisement

Hon. Nasiru Sule Garo daga Muhalli da Sauyin Yanayi zuwa Ma’aikatar Ayyuka na Musamman,

 

Hon. Ibrahim Namadi daga Kulawa da Ayyuka zuwa Ma’aikatar Sufuri,

 

Hon. Umar Haruna Doguwa daga Ilimi zuwa Ma’aikatar Albarkatun Ruwa,

 

Advertisement

Hon. Ali Haruna Makoda daga Albarkatun Ruwa zuwa Ilimi,

 

Hon. Aisha Lawal Saji daga Ma’aikatar Mata, Yara da Nakasa zuwa Al’adu da Yawon Bude Ido,

 

Hon. Muhammad Diggol daga Sufuri zuwa Kulawa da Ayyuka.

 

Advertisement

A gefe guda, Gwamnan ya sauke kwamishinoni guda biyar daga majalisar zartarwa da suka hada da:

 

Ibrahim Jibril Fagge, Ma’aikatar Kudi,

 

Ladidi Ibrahim Garko, Al’adu da Yawon Bude Ido,

 

Advertisement

Baba Halilu Dantiye, Bayani da Harkokin Cikin Gida,

 

Shehu Aliyu Yammedi, Ayyuka na Musamman,

 

Abbas Sani Abbas, Raya Karkara da Ci Gaban Al’umma.

 

Advertisement

Haka kuma, Gwamnan ya umarci Shugaban Ma’aikata da sauran kwamishinonin da akacire su kai kansu ofishin Gwamna domin yiwuwar sake ba su wasu ayyuka.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending