News
YANZU-YANZU: An tunbuke Mai Mala Buni, Gwamnan Neja, Sani-Bello, zai karbi ragamar shugabancin jam’iyyar
Daga Yasir sani abdullahi
Gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani-Bello, ya isa hedikwatar jam’iyyar APC ta kasa domin karbar mukamin shugaban jam’iyyar na riko CECPC.
Zuwan sa a yanzu yana nuni da kawo karshen shugabancin gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni a matsayin shugaban kwamitin.
A baya dai jam’iyyar APC ta bakin Sakataren CECPC, Sanata James Akpan Udohedehe, ta yi watsi da tsige Gwamna Buni a matsayin labarin karya.
Wannan tsigewar na zuwa ne makonni kadan na babban taron jam’iyyar na kasa da aka shirya yi.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
