News
Wani Jirgin Rundunar Sojin Saman Najeriya Ya Hallaka Mutane Da Dama A Sokoto
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rahotanni sun ce jirgin ya kai harin ne kan wadanda ba su ji ba, ba su gani ba, a kauyukan Gidan Sama da Rumtuwa da ke yankin karamar hukumar Silame a jihar ta Sokoto.
Bayanai sun ce jirgin yayi kuskure ne wajen kai harin inda ya zaci ko mutanen kauyukan biyu mayakan ‘yan ta’addar LAKURAWA ne.
Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un :Allah Ya Yiwa Mahaifiyar Gwamnan Jigawa Rasuwa
Wannan lamari dai ya zama ruwan dare a Najeriya , a lokuta da dama a baya Jiragen yakin rundunar sojin saman Najeriya ya sha jefa boma-bomai akan wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.
Advertisements
