Connect with us

News

Dan Bijilanti Ya Harbe Kansa Yayin Da Yake Kokarin Cafke Wani A Abuja

Published

on

Vigilante group (1)

Wani dan Bijilanti mai suna Mujahid Ibrahim, mai shekaru 32, ya harbe kansa a kafafu yayin da yake kokarin tsoratar da wani mutumi a unguwar Dei-Dei, Bwari, Abuja.

Jaridar DAILY TRUST ta ruwaito cewa lamarin ya faru da misalin karfe 12 na dare a ranar Laraba, lokacin da Ibrahim da abokin aikinsa suka tare wani mazaunin unguwar da suke gadin. A cewarsa, mutumin ya karya dokar yankin ta hana zirga-zirga bayan karfe 11 na dare.

Advertisement

A yayin kokarin tsoratar da mutumin, Ibrahim ya harba bindigarsa sama, amma daga bisani, a yayin da yake gudu, bindigar ta sake harba harsasai da suka same shi a kafafu.

Akalla harsasai bakwai aka fitar daga jikinsa, kuma yana jiran sakamakon hoto don gano ko har yanzu akwai sauran a jikinsa.

Advertisement

Abokin aikinsa, Ben Isaac, ya bayyana cewa mutumin da aka tare ya tsere, amma babban yayansa ya dauki nauyin jinyar Ibrahim. An ba shi wa’adin sa’o’i 24 don bayyana kansa ko a kama shi.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending