Connect with us

News

Kungiyar SERAP Ta Bukaci Gwamnati Ta Fara Bincike Kan Bacewar Biliyan 233 Kafin Karɓar Sabon Bashi

Published

on

tinubu 1

Kungiyar  SERAP ta bukaci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya dakatar da shirin karɓar sabon bashin dala biliyan $1.08 daga Bankin Duniya, har sai an gudanar da cikakken bincike kan bacewar Naira biliyan 233 daga hannun Kamfanin Kasuwancin Wutar Lantarki na Najeriya (NBET), da wasu ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs).

A wata sanarwa da ta fitar, SERAP ta jaddada cewa kamata ya yi gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen gano inda kudaden suka shiga, maimakon ci gaba da karɓar bashi da zai kara nauyi kan ‘yan kasa. Kungiyar ta bukaci Shugaba Tinubu da ya umurci Babban Lauyan Ƙasa, Mista Lateef Fagbemi (SAN), tare da hukumar EFCC da ICPC da su gaggauta gudanar da bincike, tare da gurfanar da duk wanda aka samu da hannu, da kuma dawo da kudaden zuwa baitul mali.

Yadda Gwamnoni 20 Suka Ƙi Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Dubu 70,000

SERAP ta bayyana cewa matakin karɓar bashi ba zai amfani ‘yan Najeriya matuka ba, musamman ganin yadda gwamnati ke kasa magance batun bacewar makudan kudade. Ta kuma ce cika gibi a kasafin kuɗi na shekarar 2025 da rage nauyin bashi zai fi amfani idan an dawo da wadancan kudaden.

A cewar kungiyar, wannan bukata ta yi daidai da tanadin kundin tsarin mulkin Najeriya da kuma ƙa’idojin ƙasa da ƙasa na yaki da cin hanci da rashawa.

Bankin Duniya ya bayyana cewa sabon bashin zai taimaka wajen inganta harkar ilimi, ƙarfafa iyalai da kuma abinci mai gina jiki ga marasa galihu. Sai dai SERAP na ganin akwai hanyoyin cikin gida da za a iya amfani da su, idan aka yi gaskiya da rikon amana.

 

Advertisement

 

 

DAILY TRUST 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending