News
Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Cimma Wata Yarjejeniya Da ASUU – Ministan Ilimi
Gwamnatin Tarayya ta karyata zargin da ake yi cewa ta kulla wata yarjejeniya da Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), inda ta bayyana cewa duk wani takarda da aka gabatar ga kungiyar na dauke ne da shawarwari, ba yarjejeniya ba.
Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Alhamis, inda ya yi karin bayani kan zanga-zangar da ASUU ke gudanarwa a sassan kasar nan.
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Dalibar Da Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya Da Kyautar Naira 200,000
A cewarsa, gwamnatin ba za ta kulla wata yarjejeniya ta bogi ko wadda ba za a iya aiwatar da ita ba, sai dai tana da niyyar cimma yarjejeniyar da za ta tabbatar da dorewar zaman lafiya a harkar ilimi.
“Gwamnatin Tarayya ba ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ASUU ba. Abin da ke akwai dai shawarwari ne da ake ci gaba da tattaunawa a kai,” in ji Ministan.
Dakta Alausa ya kara da cewa gwamnatin na ci gaba da tuntuba da shugabannin kungiyar domin tabbatar da samun mafita, tare da jaddada cewa zanga-zangar da aka gudanar kwanan nan ba za ta rikide zuwa yajin aiki ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
