Sports
Rasha na neman damar shirya gasar cin kofin Turai a 2028
Daga kabiru basiru fulatan
Rasha ta shiga cikin sahun jerin kasashen da ke gogayyar samun izinin karbar kakuncin kofin nahiyar Turai a shekarar 2028 da kuma 2032, duk da dakatarwar da ita da aka yi mata biyo bayan mamayar da tayi a Ukraine.
A ranar Laraban nan ce dai hukumar shirya wasannin nahiryar Turai ta bayyana sunayen kasashen da suka nuna sha’awar su na karbar bakuncin gasar inda kasashen Rasha da Turkiya da Ingila da kuma Ireland ne dai za su yi gogayya wajen neman karbar bakuncin gasar na shekarar 2028.
A watan Satunba ne ake saran hukumar UEFA za ta sanar da kasar da zata amshi bakuncin gasar.
Rasha ita ce dai ta karbi bakuncin gasar kwallon kafa ta duniya a shekarar 2018 sannan aka tsaida gudanar da wasan karshe na lashe kofin zakarun nahiyar Turai a wannan shekarar a can, sai dai daga baya aka sauya saboda mamayar da ta yi a Ukraine.
Turkiya na saran karbar bakuncin gasar bayan da ta yi rashin nasara a wajen Jamus da zata amsa bakuncin gasar na shekarar 2024.
-
News7 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
-
Opinion3 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion3 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
