Connect with us

News

Ƙungiyar Likitoci Ta Dakatar Da Yajin Aikin Gargadi Da Ta Shiga

Published

on

Kungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya (NARD) ta dakatar da yajin aikin gargadi da ta shiga, tare da umartar mambobinta da su koma bakin aiki daga yau Lahadi.

Shugaban kungiyar, Dr. Tope Osundara, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar da daren Asabar. Ya ce gwamnatin tarayya ta fara ɗaukar matakan amsa wasu daga cikin bukatun da kungiyar ta gabatar.

Advertisement

Rashin Shugabanci Na Gari Shi Ne Asalin Matsalar Najeriya — Sarkin II

“Wasu daga cikin bukatunmu an biya su, sauran kuma gwamnati ta yi alkawarin duba su. Mun dakatar da yajin aikin a matsayin alamar kyakkyawar niyya, domin mu sauƙaƙa wa al’ummar da ke neman lafiya a asibitocinmu,” in ji shi.

Yajin aikin ya shafi ayyukan kiwon lafiya a sassa daban-daban na ƙasar, inda rahotanni suka nuna cewa manyan likitoci da sauran ma’aikatan lafiya ne suka ɗauki nauyin kula da marasa lafiya masu tarin yawa.

Advertisement

Sai dai, har zuwa lokacin fitar da sanarwar, ba a bayyana irin bukatun da gwamnatin

ta amsa ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending