News
Ministan da PREMIUM TIMES ta bankado ya yaudari Najeriya da shaidun kammala karatu na Karya ya ajiye aiki
Bayan bincike masu zurfi da PREMIUM TIMES ta gudanar da ya fallasa ministan Kimiyya, Nnnaji da tafka cuwacuwar takardun kammala karatunsa da na NYSC, a ranat Talata, ya mika takardar ajiye aikin sa ga shugaban Tinubu.
Kakain fadar shugaban Kasa, Bayo Onanuga ya tabbatar da karbar wannan takarda in da ya yi masa fatan alkhairi a a abinda ya sa a gaba,
Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Shirin Rigakafin Kyanda Ga Yara Sama Da Miliyan 7.8 A Jihar
PREMIUM TIMES, ta bi dalla-dalla yadda Nnnaji ya rika buga shaidun kammala karatyun sa na digiri daga jami’ar Najeriya UNN, da kuma sahidar kammala aikin yi wa kasa hidima, NYSC da duk na karya ne.
Da wadannan takardu ne aka tantance shi a majalisar dattawa tun a shekarar 2023.
Nnaji da kansa ya amsa laifin cewa tabbas ba jami’ar Najeriya ba ce ta bashi wannan shaidar kammala digiri, buga abinsa yayi a kasuwa ya cigaba da harkokinsa a mastsayin wanda ya kammala digiri.
Ita kanta jami’ar ta tabbatar wa PREMIUM TIMES cewa Nnaji bai kammala karatunsa na Digiri ba, daga baya kaucewa yayi ya kama gabansa.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
