News
2023: APC ta sulhunta Goje da gwamnan Gombe, Y
Daga kabiru basiru fulatan
Kwamitin Shugabacin Jam’iyar APC na Wucin-gadi, ƙarƙashin jagorancin Mai Mala Buni ya sulhunta tsakanin Gwamna Muhammad Yahaya na Jihar Gombe da kuma abokin burmin sa na siyasa, tsohon gwamnan jihar, Sanata Ɗanjuma Goje.
Jami’in Yaɗa Labarai na Buni, Mamman Mohammed ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Laraba a Abuja.
Ya ce Buni, da Shugaban Kwamitin Sulhu na APC, Sanata Abdullahi Adamu da Kashim Shattima, mamba a kwamitin, su su ka jagoranci sulhun.
Sanarwar ta ce wannan shine karon farko da manyan ƴan siyasar na Gombe su ka haɗu tun bayan da rigimar siyasa ta ɓarke tsakanin su a shekarar bara.
Buni, wanda shine kuma Gwamnan Jihar Yobe, ya baiyana jin daɗin sa game da sulhun da a ka yi.
Ya kuma ci alwashin sulhunta duk masu ruwa da tsaki a APC domin ƙarfafa jam’iyar yayin da a ke tunkarar kakar zaɓe ta 2023.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
