Connect with us

News

Za A Fara Rajistar UTME Ranar Litinin – JAMB

Published

on

jamb exam1 (1)

Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu ta Ƙasa (JAMB) ta sanar cewa rajistar UTME 2026 za ta fara ne daga Litinin, 26 ga Janairu, zuwa 28 ga Fabrairu, a dukkan cibiyoyin kwamfuta (CBT) da hukumar ta amince da su a fadin Najeriya.

Shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana haka ne a Legas yayin taro da Kwamishinonin Ilimi na jihohi. Ya ce sayar da takardar neman rajista (e-PIN) zai fara daga 19 ga Janairu kafin fara rajistar kai tsaye.

Advertisement

Jami’an ‘Yansanda Sun Kama  Amarya Bisa  Zargin Kashe Mijinta Da Maganin Ɓera A Jigawa 

Farfesa Oloyede ya kara da cewa zaɓin jarabawar gwaji (mock) za a rufe a ranar 16 ga Fabrairu, yayin da sayar da takardun neman Direct Entry (DE) zai fara daga 2 ga Maris har zuwa 25 ga Afrilu.

Advertisement

Shugaban hukumar ya yi gargadi cewa duk cibiyoyin CBT da ba a iya sa ido a kan su daga hedkwatar JAMB ba za su samu biyan kuɗi, kuma rajistarsu a soke su.

Haka nan, ɗalibai ba su da bukatar biyan kowanne ƙarin kuɗi ga cibiyoyin CBT; kuɗin rajista da JAMB ta amince da su kaɗai ake biya.

Advertisement

 

 

Advertisement

Punch

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending