Sports
NPFL: An Ci Tarar Kano Pillars Naira Miliyan 15
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta fuskanci hukunci daga mahukuntan NPFL bayan wasu abubuwa da suka faru a wasan da ta karɓi bakuncin Rivers United a ranar Lahadi, 19 ga Afrilu, 2026.
Mahukuntan gasar sun ce ƙungiyar ta kasa samar da ingantaccen tsaro a filin wasa, abin da ya bai wa wasu mutane damar shiga wuraren da aka hana. Sun ƙara da cewa lamarin ya jefa lafiyar ‘yan wasa da jami’an wasa cikin haɗari.
JAMB Ta Fitar Da Sakamakon jarabawar UTME Na Ranar Litinin
Rahotanni sun kuma nuna cewa wasu magoya bayan ƙungiyar sun shiga cikin filin wasa ba tare da izini ba, tare da aikata halaye da suka haɗa da cin zarafi da tsoratar da jami’an wasa, lamarin da ya saba wa ƙa’idojin gasar.
Hukuncin da aka yanke
Sakamakon haka, an ci tarar ƙungiyar kamar haka:
Naira miliyan 4 saboda rashin isasshen tsaro
Naira miliyan 3 kan halaye marasa kyau da suka bata sunan wasa
Naira miliyan 3 kan rashin kula da magoya baya
Naira miliyan 3 kan cin zarafi da tsoratar da yan wasa
Naira miliyan 2 kan haddasa tsaiko da katsewar wasa
Jimillar kuɗin ya kai Naira miliyan 15.
Baya ga tara, an kuma umarci Kano Pillars da ta buga wasanni uku na gaba a gida ba tare da ‘yan kallo ba. Daya daga cikin wasannin zai gudana a wannan kakar, yayin da sauran biyun za su kasance a farkon kakar wasa mai zuwa.
Mahukuntan gasar sun ce ƙungiyar na da damar ɗaukaka ƙara cikin awanni 48 daga sanar da hukuncin.
