Connect with us

News

Iran Ta Mayar Da Martani Ga Masu Shiga Tsakani Na Pakistan Kan Shawarar Amurka Ta Kawo Ƙarshen Yaƙi

Published

on

d9cd669841cc799400b6c936a4b58e78b102c928869ded3bea1e26036a4e14b5

Iran a ranar Lahadi ta aika da martaninta ga sabon tayin Amurka na kawo karshen yaki ga masu shiga tsakani na Pakistan, in ji kamfanin dillancin labarai na gwamnati IRNA.

“An aika martanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran game da sabon tayin Amurka na kawo karshen yaki zuwa ga mai shiga tsakani na Pakistan a yau,” in ji kamfanin.

Advertisement

An Ci Tarar Ɗan Najeriya Da Matarsa Dala Miliyan 1 Kan Sare Bishiyoyi Ba Bisa Ka’ida Ba A Amurka

A cewar shawarwarin Iran, matakin tattaunawar yanzu zai mayar da hankali ne kawai kan dakatar da tashin hankali a yankin, kamar yadda wata majiya wadda ke da masaniya kan lamarin ta shaida wa IRNA, ba tare da bayyana cikakkun bayanai game da abubuwan da ke cikin martanin Iran ba.

Advertisement

Majiyoyi daga bangarori biyu sun shaida wa Reuters cewa ƙoƙarin sulhu na baya-bayan duk wani mataki ne na cim yarjejeniya ta wucin-gadi don dakatar da yaki da kuma ba da damar zirga-zirga ta Mashigar Hormuz yayin da suke tattauna wata yarjejeniya mai faɗi, wacce za ta buƙaci magance manyan matsaloli da ba su da sauƙi kamar shirin nukiliyar Iran.

Kare haƙƙoƙi

Advertisement

Iran ta jaddada cewa za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka kan matsayarta game da tattaunawa da Amurka inda take cewa kowace tattaunawa wani ƙoƙari ne na kare haƙƙoƙin ƙasa ba miƙa wuya ba.

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a ranar Lahadi ya bayyana cewa tattaunawar da ake yi da Amurka na nufin kare haƙƙin Tehran, “ba mika wuya ba.”

Advertisement

“Idan akwai maganar tattaunawa ko sulhu, ba yana nufin mika wuya ko janyewa ba, amma manufar ita ce tabbatar da haƙƙoƙin al’ummar Iran da kuma kare muradun ƙasa da ƙarfi,” in ji Pezeshkian a wata sanarwa da IRNA ta ruwaito.

Iran “ba za ta taɓa durƙusawa gaban abokin gaba ba,” in ji shi yayin wani taron ƙungiyar aikin sake gina barnar da ta haifar yayin yakin Amurka da Isra’ila.

Advertisement

Tashin hankali a yankin ya ƙaru tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kai hare-hare kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, abin da ya janyo ramuwar gayya daga Tehran kan Isra’ila da kuma abokan Amurka a yankin Gulf, tare da rufe Mashigar Hormuz.

An cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta a ranar 8 ga Afrilu ta hanyar shiga tsakani na Pakistan, amma tattaunawa a Islamabad ba ta haifar da yarjejeniya mai ɗorewa ba.

Advertisement

Daga bisani Shugaban Amurka Donald Trump ya ƙara wa wannan yarjejeniyar wa’adin da ba shi da takamaiman ƙarshe, abin da ya ba da dama ga diflomasiyya don neman warware matsalar gaba ɗaya.

 

Advertisement

 

TRT AFRIKA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending