Connect with us

News

Wani Sashe Na Ginin Babban Masallacin Zariya Ya Rufta  ‎

Published

on

1779303141432

Mutane uku sun samu raunuka bayan wani sashe na Babban Masallacin Zariya da ake ci gaba da sake gininsa ya rufta a ranar Laraba yayin gudanar da aikin zuba siminti.

‎Lamarin ya faru ne a lokacin da ma’aikata ke aikin shimfiɗa decking a bene na biyu kusa da hasumiyar kudu ta masallacin, inda wani ɓangare na ginin ya kife ba zato ba tsammani.

Advertisement

Kamfanin Maltina Ya  Ƙaddamar Da Shirin Wayar Da Kan Ɗalibai Kan Muhimmancin Karatun Kimiyya Da fasaha A Kano 

‎Shaidun gani da ido sun shaida cewa nan take aka ceto waɗanda suka jikkata tare da garzaya da su zuwa wani asibiti da ke Zariya domin samun kulawar likitoci.

Advertisement

‎Rahotanni sun tabbatar da cewa babu asarar rai sakamakon hatsarin.

‎Bayan aukuwar lamarin, an killace wurin aikin domin kauce wa wata barazana, yayin da aka ga ma’aikata suna kwashe ɓaraguzan ginin da ya rufta.

Advertisement

‎Ƙoƙarin jin ta bakin injiniyan da ke kula da aikin bai yi nasara ba, domin wasu majiyoyi sun bayyana cewa ya raka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

‎Sai dai mai magana da yawun Masarautar Zazzau, Malam Abdullahi Kwarbai, ya tabbatar da faruwar lamarin, amma ya ce masarautar ba za ta yi tsokaci a kai ba a halin yanzu.

Advertisement

‎A cewarsa, tun da farko an miƙa aikin sake gina masallacin ga wata kwamitin fasaha, wadda daga bisani ta bai wa kamfanin ginin da ke gudanar da aikin ikon kula da wurin.

‎Ya ƙara da cewa an gudanar da bikin ƙaddamar da aikin kafin fara aikin sake gina masallacin.

Advertisement

‎“Saboda haka, a yanzu masarautar ba za ta yi ƙarin bayani kan batun ba,” in ji Kwarbai.

 

Advertisement

 

DAILY TRUST 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending