News
Ko wane ne zai yi wa APC takarar mataimaki?
Dag Muhamad Muhammad Zahraddin
Sa’o’i ƙalilan ne suka rage wa jam’iyyun siyasa a Najeriya don miƙa sunayen ‘yan takararsu na shugaban ƙasa da mataimakansu ga Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa.
Jam’iyyu ƙalilan ne zuwa yanzu suka bayyana sunayen mataimakan ‘yan takararsu na shugaban ƙasa da suka fitar, yayin da mafi yawa ke ci gaba da nuƙu-nuƙu.
Tuni dai babbar Jam’iyyar adawa ta PDP ta sanar da mutumin da zai yi wa ɗan takararta Atiku Abubakar, mataimaki.
Sannan ana dakon jam’iyyar mai mulki ta APC, da sauran jam’iyyun da suka shirya shiga a fafata da su.
Masu sharhi dai na cewa muhimmancin mataimaki a siyasar Najeriya, na iya kambamawa ko ruguza tagomashin ɗan takarar shugaban ƙasa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
