Connect with us

News

Buhari Ya Nada Sabbin Ministoci

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

 

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya nada sabbin minsitoci, sa’o’i kadan bayan ’yan bindiga sun kai wa ayarin motocinsa hari a mahaifarsa Daura.

Nadin na zuwa ne sa’o’i bayan wani hari da aka kai wa Gidan Yarin Kuje da ke Abuja, inda maharan suka kashe mutum biyu a cikin ayarin.

Advertisement

Buhari ya sanar da sauye-sauyen ne a zaman Majalisar Zartarwa ta Tarayya a Fadar Shugaban Kasa ranar Laraba.

A lokacin zaman ne ya rantsar da sabbin ministocin bayan Majalisar Dattawa ta tantance su a makon jiya.

Yanzu-Yanzu: Abba Kyari, Dariye, Nyame sun tsere daga magarkamar Kuje a wani hari

Rukunin farko na sabbin ministocin da ya rantsar su ne: Henry Ikechukwu Ikoh (Abia) da Umana Okon Umana (Akwa Ibom) da Odum Odih (Ribas) da kuma Ademola Adewole Adegoroye (Ondo).

Na biyun kuma su ne: Umar Ibrahim El-Yakub (Kano) da Goodluck Nnana Opiah (Imo) da kuma Egwumakama Joseph Nkama (Ebonyi).

Kafin rantsarwar taron ya yi shiru na minti daya domin nuna jimamin rasuwar Sakatare-Janar na Kungiyar Kasashe Masu Arzikin Mai (OPEC) mai barin gado, Muhammad Barkindo, wanda ya rasu a cikin dare.

Advertisement

Rasuwar Barkindo ta auku ne a ranar da ya yi wata ganawa da Shugaba Buhari, wanda ya yabe shi a matsayin wakili abin alfahari ga Najeriya.

Barkindo ya rasu yana da shekara 63 a duniya kuma shi ne Sakatare-Janar na OPEC na hudu, daga Najeriya.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending