Connect with us

News

Gurɓataccen fetur: Majalisar Wakilan Najeriya ta nemi a dakatar da kamfanonin da ke da laifi

Published

on

Screenshot 20220204 075549
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Advertisement

Majalisar Wakilan Najeriya ta nemi gwamnatin ƙasar ta dakatar da kamfanonin mai na ‘yan kasuwa da suka shigar da gurɓataccen man fetur ƙasar.

Ƙudirin da majalisar ta cimma a yau Alhamis wani ɓangare ne na binciken da wakilan ke yi game da asalin man, wanda ya lalata ababen hawan mutane da dama a faɗin Najeriya tun daga ƙarshen watan Janairu.

Tun farko shugaban kamfanin mai na gwamnatin Najeriya NNPC, Mele Kyari, ya bayyana MRS da Oando da Duke Oil da Emadeb a matsayin kamfanonin da suka yi dakon man zuwa ƙasar daga Belgium.

Advertisement

NNPC ya ce yana ci gaba da bincike da kuma tuntuɓa don ɗaukar matakin da ya dace.

Ita ma hukumar kula da harkokin mai Nigerian Midstream and Downstream Regulatory Authority (NMDPRA) ta ce ta gano matsalar kuma tuni ta dakatar da fitar da gurɓataccen man, wanda hakan ya haddasa dogayen layi a gidajen sayar da shi.

Social embed from twitter

 

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *