Connect with us

News

Ƴan sanda sun kashe ƴan bindiga da ake zargin ƴan IPOB ne a Imo

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Rahotanni sun ce an kashe wasu da ake zargin ƴan kungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biafra IPOB ne a wani artabu da ‘yan a garin Omuma, mahaifar gwamna Hope Uzodimma da sanyin safiyar Lahadi.

An kashe ‘yan bindigar ne bayan sun kai hari ofishin ƴan sandan Omuma da ke karamar hukumar Oru ta Gabas a jihar Imo, kamar yadda CSP Mike Abattam, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Imo ya bayyana.

Ya ce ƴan bindigar sun buɗe wuta bayan sun abka ofishin ƴan sanda da safe, amma a cewarsa ƴan sanda sun murƙushe su a musayar wuta.

Jami’in ya ce mutum huɗu aka kashe yayin da wasu saura suka tsere cikin daji ɗauke harsashe a jikinsu.

Wannan na zuwa bayan wasu ƴan bindiga sun kai hari ofishin ƴan sanda a Umuguma da ke yankin Owerri ta yamma tare da kashe ƴan sanda biyu a ranar Asabar

Advertisement

Haka kuma ƴan bindiga sun kai hari gidan shugaban ƴan ƙabilar Igbo ta Ohanaeze Ndigbo inda suka ƙone gidansa.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending