News
Ƴan sanda sun kashe ƴan bindiga da ake zargin ƴan IPOB ne a Imo
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Rahotanni sun ce an kashe wasu da ake zargin ƴan kungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biafra IPOB ne a wani artabu da ‘yan a garin Omuma, mahaifar gwamna Hope Uzodimma da sanyin safiyar Lahadi.
An kashe ‘yan bindigar ne bayan sun kai hari ofishin ƴan sandan Omuma da ke karamar hukumar Oru ta Gabas a jihar Imo, kamar yadda CSP Mike Abattam, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Imo ya bayyana.
Ya ce ƴan bindigar sun buɗe wuta bayan sun abka ofishin ƴan sanda da safe, amma a cewarsa ƴan sanda sun murƙushe su a musayar wuta.
Jami’in ya ce mutum huɗu aka kashe yayin da wasu saura suka tsere cikin daji ɗauke harsashe a jikinsu.
Wannan na zuwa bayan wasu ƴan bindiga sun kai hari ofishin ƴan sanda a Umuguma da ke yankin Owerri ta yamma tare da kashe ƴan sanda biyu a ranar Asabar
Haka kuma ƴan bindiga sun kai hari gidan shugaban ƴan ƙabilar Igbo ta Ohanaeze Ndigbo inda suka ƙone gidansa.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
