Connect with us

News

DSS ta musanta kai samame wani gida a Abuja tare da sojojin Amurka

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya ta Najeriya ta yi watsi da labarin da ke cewa jami’anta ƙarƙashin hadin gwiwar sojojin Amurka sun kai samame wani gida a Abuja, babban birnin ƙasar.

 

Advertisement

Mai magana da yawun hukumar Dr. Peter Afunanya ne ya tabbatar wa kafofin yaɗa labarai wannan batu a ranar Juma’a.

Sabbin takardun Naira za su hana sayen kuri’u –kungiyoyi

Advertisement

Rahotanni sun fara yaɗuwa a farkon wannan makon cewa jami’an DSS da sojojin Amurkan sun kai samamen ne wani gida a unguwar Lugbe inda suka kama wasu mutane da ake zargin ƴan Boko Haram ne tare da abubuwan fashewa da dama.

 

Advertisement

Hakan na zuwa ne bayan da a farkon makon nan Amurkan ta fitar da sanarwa tana gargaɗin cewa akwai yiwuwar za a kai hare-haren ta’addanci a sassan Najeriya musamman Abuja.

 

Advertisement

Kafar yaɗa labaran PR Nigeria ta ruwaito Dr Afunanya yana cewa “Ina shaida mkuku cewa babu wani samame da muka kai tare da sojojin Amurka kamar yadda ake yaɗawa.

 

Advertisement

“Duk da cewa dai mun kai samame wani rukunun gidaje a Abuja tare da sauran hukumomi abokan aiki, to babu dakarun tsaron ƙasashen waje ko ɗaya a ciki,” ya ce.

 

Advertisement

PR Nigeria ta ce a wani binciken ƙwaf da ta aiwatar kan zargin dakarun ƙasashen waje sun kai samame rukunin gidaje na Trademore, ya gano cewa “babu wasu ƙwararan hujjoji cewa sojojin Amurka sun kama wani a Abuja.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending