Connect with us

News

Barazanar Harin Ta’addanci Ta Jawo Rufe Kasuwanni A Neja

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Barazanar harin ta’addanci ta tilasta masarautar Borgu da ke Karamar Hukumar Borgu ta Jihar Neja rufe manyan kasuwannin yankin.

Advertisement

 

Masauratar ta ce ta dauki wannan matakin ne domin kare rayukan jama’ar yankin daga ayyukan ‘yan ta’adda..

Advertisement

 

Abin da ya jawo faɗa tsakanin Murtala Garo da Ado Doguwa

Advertisement

Wannan na zuwa ne biyo bayan harin da ‘yan bindiga suka kai sansanin sojojin da ke Wawa, daura da tafkin Kainji, a ranar Asabar.

 

Advertisement

Cikin wata sanarwar da ta fitar ta hannun Shugaban Kungiyar Matasan yankin, Muhammad Kabir, Masarautar ta ce ganin yadda zaman dar-dar ke dada kamari a tsakanin mazauna yankin ya sa aka dauki matakin rufe manyan kasuwannin yankin don kauce wa hare-haren ta’addanci.

 

Advertisement

Kazalika, masarautar ta kafa dokar hana fita daga karfe 9:00 na safe zuwa 6:00 na yamma don takaita zirga-zirgar jama’a a yankin.

 

Advertisement

Kazalika, ta ce daga yanzu tilas masu ababen hawa a yankin su tabbatar sun yi wa ababen hawan nasu lamba ko kuma a raba su da su.

 

Advertisement

Dokar takaita zirga-zirgar da kuma umarnin tabbatar da yi wa ababen hawan lamba sun soma aiki ne daga ranar Litinin, 31 ga watan Oktoba, in ji sanarwar.

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending