Connect with us

News

Za A Yi Fama Da Hazo Da Kura A Jihohin Arewa A Kwanaki Masu Zuwa – NiMet

Published

on

Hazo da kura

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet), ta sanar da karewar yanayin damina a Arewacin kasar nan, inda ta ce wasu sassan yankin za su fuskanci yanayin kura da hazo nan da kwanaki masu zuwa.

 

Advertisement

NiMet a hasashenta ta ce kura za ta taso daga jamhuriyar Nijar kuma za ta mamaye sassan Arewacin na Najeriya.

 

Advertisement

Abubuwan da za su faru a Champions League ranar Laraba

Guguwar iska mai karfin mita 800, a cewar NiMet, za ta kai kurar zuwa Arewacin kasar nan da kuma Arewa ta Tsakiya.

Advertisement

 

Binciken ya kuma nuna cewa ana sa ran za a samu karin kura da hazo a yankin.

Advertisement

 

“A cikin sa’o’i 24 masu zuwa, akwai yiwuwar karin hazo da kura (a matsakaicin nisan zango mita 2000 – mita 5000) a jihohin Borno, Yobe, Katsina, Kano, Kaduna, Gombe, Bauchi da Jigawa, yayin da sauran jihohin Arewa (ciki har da Arewa ta Tsakiya) na iya fuskantar yanayin zafi kan mataki 5-7.

Advertisement

 

“Ana sa ran wannan yanayin zai ci gaba har zuwa kwanaki uku masu zuwa.”

Advertisement

 

NiMet ta kuma ce yawan zafin rana zai karu a hankali.

Advertisement

 

Hukumar ta shawarci masu ababen hawa da su rika yin tuki cikin natsuwa a wannan yanayi.

Advertisement

 

“Hakanan mutanen da ke da matsalar numfashi ya kamata su yi taka tsantsan, musamman a lokutan da suke waje,” inji NiMet.

Advertisement

 

Ta kuma shawarci ma’aikatan jirgin sama da su nemi sabbin rahotannin yanayi daga ofisoshinta don inganta ayyukansu.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending