News
An nada alkalan da za su saurari korafe-korafen zabukan 2023 a Najeriya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Alkalin alkalan Najeriya mai shari’a Olukayode Ariwoola ya rantsar da alkalan da za su jagoranci sauraron korafe-korafen zabukan kasar na 2023
An yi bikin rantsar da alkalan ne ranar Litinin a harabar hukumar da ke kula da harkokin shari’a ta kasar a Abuja babban birnin kasar
Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Zai Dawo Aiki A Watan Nuwamba
Yayin da yake nada alkalan babban alkalin alkalan kasar ya umarce su, da su dauki aikinsu da matukar muhimmanci, yana mai gargadinsu da cewa ba zai lamunci wasa da aiki ba.
Daga cikin wadanda suka halarci taron har da shugabar kotun daukaka kara ta kasar mai shari’a Monica Dongban-Mensem, da shugaban hukumar zaben kasar Farfesa Mahmood Yakubu, da kuma sauran alkalan kotun daukaka kara ta kasar.
