Connect with us

News

Kasurgumin Dan Bindiga Ya Shiga Hannu Bayan Shekara 7 Ana Farautarsa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rundunar ‘yan sandan Jihar Anambra ta tabbatar da cafke wani mutum mai suna Matthew Nwankwo, wanda ake zargin shugaban wata kungiyar masu garkuwa da mutane ne, shekara bakwai bayan ayyana ana nemansa ruwa a jallo.

 

Advertisement

Tun a 2015 ne Nwankwo ya tsere lokacin da gwamnatin Anambra ta rushe gidansa da ke kauyen Umuobindo a garin Nteje na Karamar Hukumar Oyi bayan da aka gano yana amfani da gidan a matsayin maboyar mutanen da suka yi garkuwa da su.

 

Advertisement

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano ta janye dokar hana ƴan adaidaita-sahu bin wasu tituna

‘Yan sanda sun kama wanda ake zargin ne da sanyin safiyar ranar Talata, bayan da jami’an tsaro suka samu bayanan sirri kan maboyarsa.

 

Advertisement

DSP Toochukwu Ikenga, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ya tabbatar da damke wanda ake zargin.

 

Advertisement

“Wanda ake zargin yana tsare, ana ci gaba da bincike a kansa,” in ji shi.

 

Advertisement

A cewar kakakin, kasurgumin dan bindigar da yaransa sun addabi jihar da kewayenta wajen fashi da makami da kuma garkuwa da mutane.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending