Connect with us

News

Mutum 61 Suka Mutu A Hatsarin mota A Borno —Hukuma

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC), ta ce mutum 61 suka mutu a haddura 33 da suka auku a sassan Jihar Borno tsakanin watan Mayu da Nuwamba, 2022.

Advertisement

 

Kwamandan hukumar a jihar, Utten Iki-Boyi ne ya bayyana hakan ranar Alhamis a Maiduguri, babban birnin jihar.

Advertisement

 

Wata mata a Amurka ta yi kokarin bude kofar jirgin sama ana tsaka da tafiya

Jami’in ya ce, daga cikin hadurran da suka auku, mutum 151 sun jikkata.

Advertisement

 

Ya kara da cewa, baki daya hadurran sun rutsa da mutum 285 ne da kuma motoci 46.

Advertisement

 

Ya ce, a Nuwamban da ya gabata mutum 37 ne suka mutu a hadurran da aka samu a hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.

Advertisement

 

Iki-Boyi ya danganta aukuwar hadurran da gudun wuce kima da tukin ganganci da amfani da taya mara inganci da sauransu.

Advertisement

 

Daga nan ya gargadi masu ababen hawa, musamman masu motocin haya, da su rika amfanai da tayoyi masu inganci tare da kula da abubuwan hawansu yadda ya kamata.

Advertisement

 

(NAN).

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending