Connect with us

News

An Rage Kudin Karatun A Jami’o’i A Legas

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya sanar da rage kashi 65 cikin 100 na kudin karatu a jami’o’in jihar.

 

Advertisement

Tokunbo Wahab, mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin ilimi ne ya bayyana hakan da safiyar ranar Alhamis.

 

Advertisement

Yawan waɗanda zazzaɓin maleriya ke kashewa ya ragu a bara – WHO

Wahab, ya ce gwamnatin za ta ci gaba da bayar da tallafi ga jami’o’inta tare da sanya su cikin yanayi mafi inganci a Najeriya.

 

Advertisement

Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Legas (LASUSTECH) da Jami’ar Ilimi ta Jihar Legas (LASUED) na daga cikin wadanda za su amfana da wannan tagomashi.

 

Advertisement

 

Mahukuntan jami’o’in sun bayar da shawarar mayar da kudin makarantun zuwa Naira 195,000 kafin rage shi zuwa kashi 65% da Gwamna Sanwo-Olu ya sanar.

Advertisement

 

Shugaban Kungiyar Dalibai (SUG) ta Kwalejin Ilimi ta Adeniran Ogunsanya, Okeychukwu David, ya ce ya ji dadin wannan labari.

Advertisement

 

Gwamnan ya bayar da tabbacin duba yanayin rayuwa da ake ci don tallafa wa bangare ilimin jihar, don ganin dalibai sun samu ingantaccen ilimi da zai amfani al’ummar jihar da ma kasa baki daya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending