Connect with us

News

Sojin Najeriya sun musanta zargin zubar wa mata ciki a Borno

Published

on

Manjo Janaral Jimmy Akpor

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Shalkwatar tsaro ta Najeriya ta mayar da martani kan rahoton kamfanin dillancin labarai na Reuters wanda ya zargi sojojin ƙasar da aiwatar da wani shirin zubar wa matan da mayaƙan Bpoko Haram suka yi wa fyaɗe ciki.

Advertisement

 

Shalkwatar tsaron ta bayyana rahoton na Reuters a matsayin labarin kanzon kurege.

Advertisement

Masu Shigo Da Jabun Magunguna Kano Sun Gurfana A Kotu

Tare da cewa wani shiri ne na shafa wa sojojin Najeriyar kashin kaji.

 

Advertisement

Shugaban sashen yaɗa labaru na shalkwatar tsaron Manjo Janaral Jimmy Akpor ya ce tun daga watan Yulin 2021 har zuwa watan Nuwamban bana mayaƙan Boko Haram sama da dubu 82 tare da iyalansu ne suka yi saranda ga dakarun ƙasar kuma fiye da dubu arba’in daga ciki yara ne.

 

Advertisement

Ya kuma ƙara da cewa gwamnatin jihar Borno ta samar wa tsoffin mayaƙan Boko Haram da iyalan nasu matsugunai domin ba ta son ta raba yaran da iyayensu.

 

Advertisement

Shalkwatar tsaron ta kuma ƙara da cewa an haifi jarirai 262 a cikin wannan sansani, cikin watanni huɗu.

 

Advertisement

Rahoton na kamfanin dillancin labaru na Reuters ya yi zargin cewa an tilasta wa mata da yara mata dubu 12 zubar da ciki tun daga 2013 karkashin wani shiri da aka aiwatar cikin sirri.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending