Connect with us

News

NAFDAC Ta Kwace Jabun Magunguna Na N20m A Kasuwar Zariya

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), ta kama tare da kwace jabun magunguna na kusan Naira miliyan 20 a Jihar Kaduna.

Advertisement

 

Kamen wanda hukumar ta yi a ranar Litinin, ya hada ne da magungunan da ba su da rajista da kuma wadanda wa’adin aikinsu ya kare.

Advertisement

 

Asusun lamuni na duniya zai bai wa Ghana taimakon dala biliyan uku

NAFDAC ta kwace magungunan ne a tsakanin shaguna 26 da ke Kasuwar Sabon Gari cikin Karamar Hukumar Zariya da ke jihar.

Advertisement

 

Magungunan sun hada da wadanda aka tanadar don raba wa ‘yan gudun hijira kyauta a jihar da wadanda akan bai wa mata masu nakuda da sauransu.

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar ta ce da damar maganin ya lalace ne saboda rashin samun ajiyar da ta dace.

 

Advertisement

Da yake yi wa manema karin haske, Mataimakin Darakta na Sashen Bincike na NAFDAC reshen jihar ta Kaduna, Tamanuwa Andrew, ya ce, wannan bangare ne na kokarin da hukumar ke yi wajen yaki da jabun magaunguna a kasar nan.

 

Advertisement

(NAN)

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending