Connect with us

News

Karya Ta Kashe Matashi A Kano

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata mahaukaciyar karya ta hallaka wani matashi mai suna Faruk Usman bayan ta gantsara masa cizo da wasu abokansa hudu a Jihar Kano.

 

Advertisement

Dan uwan marigayin da ya yi jinyar sa, Saddiku Usman, ya ce mutum guda daga cikin abokan yana kwance a asibiti, sauran kuma suna karbar magani.

Rikici ya tilasata wa dubban ‘yan Sudan Ta Kudu guduwa Sudan

 

Advertisement

Saddiku ya ce, “Ni nake jinyar sa, ya kuma ce min sun tare karyar ne a titi suna kokarin rike ta, bayan mai ita ya zo karba, sai kawai ta hau cizon sa da wasu abokansa hudu.”

 

Advertisement

Tashar Freedom Radio Kano ta ruwaito Saddiku yana cewa likitoci sun shaida musu cewa jinkirin zuwa asibiti ne ya yi sandiyar rasuwar dan uwan nasa.

 

Advertisement

 

Lamarin dai ya faru ne a unguwar Dan Agundi Layin Maigasara da ke Karamar Hukumar Birni a Jihar Kano kuma tuni aka yi jana’izar matashin.

Advertisement

 

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce akalla mutane 55,000 ne ke mutuwa kowace shekara sakamakon kamuwa da cutar cizon mahaukacin kare da sauran cututtuka masu alaka da hakan da ke yaduwa da kashi 99 cikin 100.

Advertisement

 

WHO ta ce rashin bai wa cutar muhimmaci da al’umma ke yi ne ya sanya adadin ke kara karuwa duk shekara a Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending