News
2023: ’Yan Siyasa Ne Ke Murde Zabe Ba Mu Ba – INEC
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), ta ce babu ruwanta da murdiyar zabe amma ’yan siyasa ne ke aikata hakan.
Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Kwamishinar hukumar ta Jihar Ebonyi, Onyeka Ugochi, yayin ganawarta da manema labarai da kungiyoyi a jihar.
Ta ce, “INEC ba ta murdiyar zabe, ’yan siyasa ne ke aikata haka.”
Onyeka ta ce babu wata kafa da hukumar za ta bari wadda za ta ba da damar murdiyar zabe a 2023.
Ta kara da cewa, murde zabe a wannan karo abu ne mai wahalar gaske saboda kyakkyawan shirin da hukumar ta yi wa manyan zabukan 2023.
A cewarta, hukumar za ta yi iya yinta wajen tabbatar da sahihin zabe, kuma ba za ta bari kowane irin matsin lamba daga ko’ina ya yi tasiri a kanta ba.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
