News
Gobara Ta Yi Ajalin Yara 3, Ta Lalata Dukiya A Yobe
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA), ta ce ta samu rahoton mutuwar yara uku a wata gobara da ta tashi a garin Nguru na jihar.
Yayin da aka shiga yanayin sanyi, hukumar ta gargadi jama’ar jihar da yin taka tsan-tsan wajen amfani da wuta, da sauran na’urorin lantarki.
Kifewar kwale-kwale: An sake gano gawar mutum biyar a Jihar Kebbi
“SEMA na son yin amfani da wannan kafa wajen yin kira ga shugabannin al’umma da magidanta da su yi taka-tsan-tsan a wannan lokaci, ta hanyar tabbatar da cewa an kashe duk na’urorin lantarki idan ba a amfani da su ba, a kashe itacen wuta yadda ya kamata bayan an kammala amfani da su.”
Hukumar ta bayyana hakan ne a wani sako da ta wallafa ta shafinta na Facebook ranar Alhamis.
SEMA ta kuma bayyana cewa ta samu rahoton afkuwar gobara a kananan hukumomin Damaturu da Fune a tsakanin ranakun 28, 30 ga Disamba, 2022 da kuma 4 ga Janairu, 2023.
Binciken da SEMA ta gudanar ya nuna yadda aka yi asarar dukiya kama daga kan gidaje, kayan abinci da sauransu.
Hukumar ta ce tana kokarin tallafa wa wadanda lamarin ya shafa don rage musu radadin halin da suke ciki.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
