Connect with us

News

Makomar tallafin man fetur a Najeriya bayan Yunin 2023

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa zuwa Yunin 2023, za ta daina biyan kuɗin tallafin fetur da ta saba biya.

 

Advertisement

Ministar kuɗi da kasafi ta ƙasar Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a lokacin da ta ke gabatar da kasafin na 2023 ga jama’ar ƙasar.

Ya kamata Gwamnatin Tarayya Ta Gaggauta Janye Karin Kudin Wutar Lantarki – SERAP  

Ta bayyana cewa a 2023, gwamnatin ta ware naira tiriliyan 3.36 ne kawai domin biyan tallafin fetur na wata shidan farko na shekarar.

Advertisement

 

Ta kuma ce wannan matakin na tafiya ne da ƙarin wa’adi na watanni 18 na cire tallafin da aka sanar a 2022.

Advertisement

 

A lokacin da take bayani kan gundarin kasafin, ministar ta bayyana cewa kuɗin shigar da ƙasar ke samu zuwa Nuwambar 2022 ya kama tiriliyan 6.5, wanda hakan ke nufin ya kusa kai adadin da ƙasar ke da burin samu a bana na tiriliyan 7.8

Advertisement

 

Ministar kuma ta bayyana ɗaya daga cikin masu kawo wa ƙasar kuɗin shiga akwai naira biliyan 586 wanda ita da kanta gwamnatin tarayya ke samarwa sai kuma hukumar kwastam ta ƙasar mai kawo naira biliyan 15.

Advertisement

 

Haka kuma akwai harajin da ake karɓa daga jama’a wanda ya kai tiriliyan 1.3 da kuma tiriliyan 3.7 da ake karɓa daga sauran ɓangarori.

Advertisement

 

Manyan ɓangarorin da suka tallafa wa tattalin arziƙin ƙasar a 2022 akwai ɓangaren noma wanda ya samar da kashi 23 cikin 100 da kuma ɓangaren sadarwa da kasuwanci da man fetur da suka bayar da kashi 5.6.

Advertisement

 

Raguwar da ake samu na tallafin da fetur ke bai wa ƙasar ya sa gwamnatin ƙasar ta yanke shawarar samun hanyoyin kuɗin shiga ga ƙasar.

Advertisement

 

Sai dai a halin yanzu, gwamnatin Shugaba Buhari za ta miƙa mulki ga sabuwar gwamnati a Mayun 2023 bayan zaɓen da za a gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Advertisement

 

Babbar tambayar a nan ita ce mece ce matsayar waɗanda suke takarar shugabancin Najeriyar a game da tallafin man fetur?

Advertisement

 

Atiku Abubakar

Advertisement

Atiku Abubakar wanda shi ne ɗan takarar shugabancin Najeriya a Jam’iyyar PDP ya bayyana cewa zai cire tallafin man fetur sa’annan kuma ya karkatar da kuɗin ta ɓangaren sufuri da kuma ilimi.

 

Advertisement

“Duk wasu kuɗi da muke samu muna ɗaukar su domin biyan bashi. Idan da za mu ɗauki matakai masu kyau, za mu iya samun kuɗi masu yawa da za su taimaka a yi manyan ayyuka da biyan albashi da na gudanarwa,” in ji Daniel Bwala, mai magana da yawun yaƙin neman zaɓen Atiku kamar yadda ya shaida wa wata kafar watsa labarai ta Najeriya.

 

Advertisement

Atiku ya bayyana cewa tallafin fetur shi ke lashe kashi 60 cikin 100 na bashin da Najeriya ke biya a duk shekara.

 

Advertisement

“Za mu iya samun kuɗi masu yawa domin zuba jari a ɓangaren wuta da man fetur da ilimi idan muka cire tallafi,” in ji shi.

Bola Tinubu

Advertisement

Ɗan takarar shugabancin Najeriya a Jam’iyyar APC mai mulki Bola Ahmed Tinubu shi ma ya bayyana cewa ba gudu ba ja da baya kan batun cire tallafin man fetur.

 

Advertisement

Tinubu ya bayyana cewa kowace irin zanga-zanga jama’a za su yi, ba zai jingine aniyarsa ta cire tallafin fetur din ba.

 

Advertisement

“Ta ya za a biya tallafin man fetur ɗin da ake sha a Kamaru da Nijar da Jamhuriyyar Benin. Duk irin zanga-zangar da za ku yi, sai mun cire tallafin man fetur,” in ji shi.

 

Advertisement

Ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar APC ya ce gwamnatinsa za ta bayar da dama ga kamfanoni masu zaman kansu su wataya ba tare da saka musu ido ba inda ya ce hasali ma zai taimaka musu ne.

 

Advertisement

Peter Obi

Shi ma ɗan takarar shugabancin Najeriya a Jam’iyyar LP Peter Obi ya caccaki tsarin Najeriya na biyan tallafin man fetur.

Advertisement

 

Peter Obi ya sanar da cewa ya yanke shawarar kawo ƙarshen wannan matakin ta hanyar tura kuɗaɗen ta ɓangaren wutar lantarki da kiwon lafiya da ilimi idan aka zabe shi a 2023.

Advertisement

 

Ya kuma ƙara da cewa irin adadin kuɗin da aka kashe kan tallafin man fetur a shekara 12 da suka wuce ya isa ya magance matsalolin da ake da su a ƙasar da suka haɗa da na ilimi da kiwon lafiya da ɓangaren lantarki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending