Connect with us

News

Za mu haɗa hannu da EFCC domin hana sayen ƙuri’a a zaɓen bana – INEC

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya INEC ta sha alwashin magance matsalar sayen ƙuri’a a zaɓen ƙasar da ke tafe, ta hanyar haɗa hannu da hukummomin da ke yaƙi da cin hanci da almundahar kuɗade na ƙasar ICPC da EFCC.

 

Advertisement

Hukumar ta bayyana sayar da ƙuri’a a matsayin ”tsutsar” da ke yi wa harkokin siyasar ƙasar tarnaƙi.

Buhari zai tafi Senegal taron harkokin noma

Kwamishinan hukumar mai lura da jihar Rivers Johnson Alalibo Sinikiem, ne ya bayyana haka ranar Litinin a birnin Fatakwal a lokacin da ya halarci taron da ƙungiyar ‘yan jarida ta ƙasar ta shirya.

Advertisement

 

Mista Sinikiem ya ce hukumar ta sha wayar da kan matasan ƙasar musamman a yankunan karkara da su lura tare da kai rahoton duk wanda suka samu da laifin saye da sayar da ƙuri’a a lokacin zaɓukan ƙasar da ke tafe.

Advertisement

 

A ranar 25 ga watan Fabrairu ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending