Connect with us

News

A ƙarshe, Ganduje ya kori Muhuyi Magaji

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

A karshe dai gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya kori dakataccen shugaban hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimingado.

 

Advertisement

Tun a watan Yulin 2021 Gwamnatin jihar ta dakatar da Rimingado, jim kadan bayan ya bude bincike kan kwangilolin da ake zargin an baiwa kamfanonin da ke da alaka da iyalin gwamnan.

Hisbah Ta Fara Binciken Matar Da Ta Auri Saurayin Ƴarta A Kano

Wata wasika da sakataren gwamnatin jihar, Usman Alhaji ya aikewa Rimingado, ta ce gwamnan jihar ya dogara ne da kudurin majalisar dokokin jihar a watan Yulin 2021 na tsige shi daga mukaminsa.

Advertisement

 

“Korar ta biyo bayan tanadin sashe na 6 na dokar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008 kamar yadda aka yi wa kwaskwarima.

Advertisement

 

Da aka tuntube shi domin jin ta bakinsa, Mista Rimingado ya soki matakin da gwamnan ya dauka, yana mai cewa gwamnati ta ƙi yin biyayya ga hukuncin kotun masana’antu ta kasa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending