Politics
PDP Ce Ta Haifar Da Wahalar Man Fetur A Najeriya – Tinubu
DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya ce dillalan man da PDP ta bai wa lasisi zamanin mulkinta ne ke boye fetur yanzu a Najeriya.
Tinubu ya kuma ce magoya bayan PDPn da jam’iyyar ta bai wa lasisin zamanin mulkinta ne ke yin hakan saboda dalilan siyasa da kuma haddasa dogayen layuka a gidajen mai.
Ana tuhumar yaro ɗan shekara 13 da fyaɗe da cin zarafin mata
Tinubu ya bayyana hakan ne yayin taron yakin neman zabensa da ya gudanar a Binuwai.
“PDP Jam’iyya ce ta ruruta wutar talauci ce, musamman idan aka yi la’akari da yadda ’yan Najeriya ke shan bakar wahala a yanzu.
“Sun bai wa magoya bayansu lasisin da yanzu ya haifar da dogayen layi na jabu a gidajen mai. PDP haka ya ishe ku fa!
Ya kuma rashin sanin doka ne ya sanya abokin hamayyarsa Atiku Abubakar, ya ce kasuwancin sufuri yake a lokacin da yake aiki da Hukumar fasa kauri ta kasa, lokacin da yake amsa tamabayar da wasu su ka yi masa kan yadda yayi arziki haka.
“Suka tambaye shi ya aka yi yayi arzikin d ayake da shi, ya kada baki ya ce kasuwancin sufuri yake. Bai san cewa laifi ne babba ba a ce ka na ma’aikacin gwamnati kuma kayi wani aikin ba noma ba.
Tinubu ya kuma ce yana da yakinin yadda ya ciyar da jiharsa ta Legas gaba, zai tabbatar yayi wa Najeriya haka.
