News
An Ceto Yarinyar Da Aka Sayar N100,000 A Kaduna
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
An ceto wata yarinya ’yar shekara shida wadda aka sace aka kuma sayar da ita N100,000 a Jihar Kaduna.
Rundunar ’yan sandan jihar ta ce bayan samun rahoton bacewar yarinyar ranar 23 ga Janairu, jami’anta suka sunkuya bincike wanda a karshe aka kama wata makwabciya da ake zargi da hannu a bacewar ’yar.
“A halin bincike an sake kama wani mutum da wata mata da suke da hannu a bacewar yarinyar,” in ji rundunar.
Ta kara da cewa an kubutar da yarinyar ce ba tare da wani rauni ba bayan kuma an sayar da ita a kan N100,000.
Aminiya ta rawaito cewaTuni dai aka sake hada yarinyar d a iyayenta.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
