News
Zaben 2023: Tinubu Ya Yi Nasara A Ogun, Atiku A Matsayi Na Biyu
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe zaben shugaban kasa a jihar Ogun, inda ta doke jam’iyyar PDP da sauran jam’iyyun siyasa.
A cewar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a jihar Ogun, dan takarar jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya zo na daya da kuri’u 341,554, yayin da Atiku Abubakar na PDP ya samu kuri’u 123,831.
A matsayi na uku, na hudu da na biyar, Peter Obi na Labour Party (LP) ya samu kuri’u 85,829, Dumebi Kachikwu na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) da 10,529, sai Rabiu Kwankwaso na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) 2,200.
Adadin masu kada kuri’a a jihar ya kai 2,687,606 inda jimillan wadanda aka amince da su ya kai 612,341.
Adadin kuri’un da aka kada ya kai 611,448, wanda ya kunshi sahihin kuri’u 580,124 da kuri’u 31,324 da aka ki amincewa.
Channel
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
