News
Wasu Yan bindiga sun kashe masarauci a Kano
Wasu ƴan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe Maigarin Kauyen karamar hukumar Rimingado, Alhaji Dahiru Abbas, a yau Lahadi.
Marigayi Abbas shine mahaifin Barista Munir Dahiru, Ciyaman ɗin karamar hukumar Rimingado.
Kotun ƙoli ta ce a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗi
Wata majiya daga iyalin mamacin ta shaida wa manema labarai a Kano cewa maharan da har yanzu ba a san ko su waye ba sun kai farmaki gidan marigayin da ke kauyen Maigari da sanyin safiyar Lahadi.
Majiyar ta bayyana cewa a lokacin da ƴan bindigar suka zo sun yi wa marigayin raunuka daban-daban kafin daya daga cikinsu ya harbe shi har lahira.
Majiyar ta shaida wa manema labarai cewa za a yi jana’izar sa da karfe 10 na safiyar yau Lahadi a gidan marigayin.
Wakilinmu ya kira kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, amma wayarsa a kashe.
Ya aika masa da sakon kar-ta-kwana amma har zuwa lokacin hada wannan rahoto babu amsa.
