Connect with us

News

Kanawa 10 ’Yan Uwan Juna Sun Mutu A Hatsarin Mota A Kaduna

Published

on

Wasu mutum 10 ’yan uwan juna sun mutu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyar Kaduna zuwa Kachia a yayin da suke dawowa daga daurin aure a Jihar Kano.

 

Hatsarin ya faru ne a yammacin ranar Litinin, bayan motarsu ta yi karo da wata motar ice.

Advertisement

 

NBC ta haramta sanya batutuwan addini da na ƙabilanci a shirye-shiryen siyasa

Wani mazaunin Kachia, Isiyaku Musa Kachia, ya shaida wa Aminiya cewa, dukkan wadanda suka rasu Kanawa da ke zaune a garin Kachia.

Advertisement

 

Ya ce: “Sun je garinsu Kano ne daurin aure, a hanyarsu ta konawa Kachia, motar Golf da suke tafiya a ciki ta yi karo da wata babbar motar ice, su 10 da ke cikin motar duka suka mutu nan take.”

Advertisement

 

 

Advertisement

Ya ce an yi jana’izarsu kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a Kachia.

 

Advertisement

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) a Jihar Kaduna, Zubairu Mato, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya danganta hatsarin da tsinkewar birki.

 

Advertisement

Ya ce motar kirar Golf ta yi lodi fiye da kima a lokacin da hatsarin ya auku, kuma daga cikin wadanda abin ya shafa akwai maza manya takwas da yara maza biyu.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending